🌿 Ruzu Non-Alcoholic Herbal Bitters
Ruzu Non-Alcoholic Herbal Bitters is a natural health supplement specially formulated to:
- ✅ Promote general wellness
- ✅ Detoxify the body
- ✅ Support the treatment of various ailments
Made from a powerful blend of 100% organic and medicinal herbs, Ruzu is completely alcohol-free, making it ideal for:
- 👪 All age groups
- 🌱 Health-conscious individuals
- 🌿 Anyone seeking non-alcoholic herbal remedies
Whether you're looking to boost your vitality, cleanse your system, or support healing the natural way, Ruzu Bitters offers a trusted herbal solution.
Hukumar Zabe Ta Kananan Hukumomi ta Jihar Osun (OSSIEC) ta bayyana shirin daukar ma’aikata fiye da 8,000 na wucin gadi don zaben kananan hukumomi da aka tsara a yi a ranar 22 ga Fabrairu, 2025.
A cewar shugaban OSSIEC, Mista Hashim Abioye, wanda ya yi magana a ranar Alhamis a ofishin hukumar dake Osogbo, ya tabbatar da cewa shirye-shiryen zaben suna cikin matakin karshe.
Ya jaddada ‘yancin hukumar, inda ya bayyana cewa Gwamna Ademola Adeleke bai yi tasiri a cikin ayyukan hukumar ba.
A lokacin da mambobin Kwamitin Majalisar Dokokin Jihar Osun kan Kananan Hukumomi, karkashin jagorancin Mista Olujinmi Asagade, suka ziyarci, Abioye ya bayyana kokarin hukumar wajen tabbatar da cewa zaben zai gudana cikin sauki.
“Game da shirye-shiryenmu na zabe, zan iya cewa muna cikin cikakken shiri. Muna amfani da fasaha wajen daukar ma’aikatan wucin gadi domin tabbatar da ingantaccen tsarin aiki. Idan bamuyi hakan ba, za a cika dakinmu da taron jama’a.
“Za mu bukaci sama da ma’aikata 8,000 na wucin gadi don zaben,” in ji shi.
Abioye ya kuma bayyana cewa an kafa dandalin yanar gizo mai aiki domin daukar ma’aikata da sauran ayyukan shirye-shirye.